17 Satumba 2014 - 09:17

Kimanin Mutane 9 suka rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata sanadiyar ci gaba da gumurzu tsakanin ‘yan bindiga da Sojojin khalifa Haftar a kasar Libiya. Kamfanin dinlancin Labarai na Reuteus ya habarta cewa a kokarin da ‘yan bindigar kasar Libiya keyi na amshe filin sabka da tashi na filin jirgin saman birnin Bangazi sun hadu da tirjiya na Sojojin kasar masu biyayya ga tsohon janar Khalifa haftar wanda hakan yayi sanadiyar mutuwar ‘yan bindigar guda 9 tare da jikkatar wasu da dama daga cikinsu.

Wata majiyar kai agaji a birnin na Bangazi ta ce a wannan sabon yunkuri da ‘yan bindigar suka sake kaiwa kimanin Mutane 30 sun samu mumunan rauni daga cikinsu.

Daga nashi waje Sakar Jarushi wani komandan sojojin Sama na kasar ya tabbatar da wannan labari, sannan ya ce har yanzu babban filin tashi da sabka na jiragen saman birnin Bangazi na kalkashin ikon Sojoji masu biyayya ga khalifa haftar tsohon janar mai ritaya. ABNA